06/08/2026
Muna kiran alkawari da Allah ya yi da Adamu Alkawarin Ayyuka domin biyayyar mutum ita ce hanyar da za a sami albaarkar alkawarin. Idan Adamu ya yi biyayya ga Allah ta wurin cika umurinsa – ya hayayyafa, ya mallaki duniya yadda Allah ya umarta, kuma ya guji cin daga itacen da aka hana – da ya sami rai na har abada. Haka kuma, zuriyarsa ma da sun amfana da wannan albarka. (Far. 1:28; 2:15–17).



