
Menene Alkawarin Ayyuka?
06/08/2026
A Lokacin da Nake Jin Nake Jin Kamar Na Tsaya Cik
13/08/2026Wuri Mafi Tsarki
“Domin in zauna a tsakiyarsu” (Fit. 25:8). Alfaruwar sujada ta Isra’ila wani gagarumin aikin gine-gine ne mai ban al’ajabi. Dukkan manufarta ita ce bayyanar da gagarumar kasancewar Allah marar iyaka a fili. Kafin a gina ta, kasancewar Allah ya bayyana a lokuta daban-daban, a wurare daban-daban, kuma ta hanyoyi daban-daban. Ga Adamu da Hauwa’u, Ya bayyana Kansa sa’ad da suka “ji muryar Ubangiji Allah yana tafiya a cikin gonar” (Far. 3:8). Ga Ibrahim Ya bayyana Kansa a matsayin tukunyar wuta mai hayaƙi da fitila mai cin wuta (Far. 15:17). Ga Yakubu Ya bayyana Kansa a matsayin mutumin da Yakubu ya yi kokuwa da shi (Far. 32:22–32). Ga Musa Ya bayyana Kansa a matsayin kurmi mai cin wuta wanda ba a cinye shi ba (Fit. 3:2). Kuma ga dukan Isra’ila Ya bayyana Kansa a matsayin al’amudin girgije da rana da kuma al’amudin girgije wuta da dare (13:21–22) a lokacin tafiyarsu ta jeji, da kuma a matsayin giza-giza mai kauri, walƙiya da tsawa, da ƙarar ƙaho (Fit. 19:9, 16).
Duk da haka, game da alfaruwar akwai wani sabon abu. Kasancewar Allah bai ƙara zama kamar baƙo mai zuwa da tafiya ba, sai dai kamar mazauni wanda ya zauna a cikin tanti kamar yadda suke, a tsakiyarsu. Don haka, alfaruwar ita ce gidan sarautarsa, wadda ta cika da ƙofa a cikin labule, da labulen da suka kewaye ta, da teburin gurasa, da fitila don haske, da kuma sunduƙin alkawari a matsayin matashin ƙafafunsa na sarauta.
Wani fanni na wannan sabon abu shi ne, yanzu, mutanen alkawari za su iya more kasancewar Ubangiji a tsakiyarsu ta hanyar da kakanninsu ba su samu ba. Kuma wannan yana da matuƙar amfanin koyarwa ga Kiristoci a yau ma, tun da yake alfaruwar ita ce alamar mazaunin Allah a tsakaninmu a cikin jiki:
Kuma Kalmar ta zama jiki, ta kuma zauna [kalmar zauna ana iya fassara ta da “ya yi alfarwa”] a tsakaninmu, mun kuma ga darajarsa, daraja kamar ta Makaɗaicin Ɗa wanda ya fito daga Uba, cike da alheri da gaskiya. (Yohanna 1:14)
Kasancewar Ubangiji za a iya more ta ne kawai bisa sharuɗɗansa. Ya bayyana waɗannan sharuɗɗan ga Musa, yana cewa, “Daidai kamar yadda na nuna maka game da samfurin alfaruwar, da na dukan kayayyakinta, haka za ku yi shi” (Fit. 25:9). Filla-fillan bayanin labarin (daga sura 25–30) ya nuna mana wannan sosai. Allah yana bayyana kansa gare mu, mutanensa, kuma ta hanyar Maganarsa za mu iya kusantar sa, mu kuma san shi. Yayin da muke kiyaye duk abin da Ubangiji ya umarce mu a koya mana ta wurin masu hidimar Maganarsa, za mu iya tabbata cewa yana “tare da [mu] kullum, har zuwa ƙarshen zamani” (Mat. 28:19–20).
Mutane sun ji dadin kasancewar Ubangiji domin ya bayyana kansa, kuma ya yi aiki ta wurin bayinsa da ya zaba, wato firistoci. Dukan Isra’ila suna iya gani, ji, da kuma gane hidimarsu, domin su ne masu hidimar kasancewar Ubangiji a tsakaninsu. Tufafin firistocin ma an yi su ne domin su nuna wa mutanen Allah daukaka da kyawun Ubangiji. (Fit. 28:2). Kuma sun miƙa hadayu domin zunuban mutane na ganganci da na rashin sani, domin kafara da kankara na zunubansu, da kuma nuna godiya ga ayyukan alherin Allahnsu (Lev. 1–7). A gaskiya ma, ɗaya daga cikin abubuwan ban sha’awa game da tsarin hadaya shi ne yadda mutane suka sa hannu a ciki. Mutane sun kawo nasu dabbobin don a miƙa hadaya, suka ɗora hannayensu a kan kan dabbobin, suka kuma bayyana nasu zunuban. Bugu da ƙari, game da hadayar da aka sani da hadayar salama, ba wai kawai Ubangiji ya “ci” nasa kason a kan bagadi ba kuma firistoci suka sami nasu kason, har ma mutanen sun ci wani kason nata (Lev. 7:11–18).
Ubangiji ya ba wa mutanensa alfarwar domin ta hanyar Maganarsa, da alamun sakalamenti na alheri da ke cikin firistoci da hadayu, da kuma addu’o’in da aka miƙa a can, ya zauna a tsakaninsu cikin alheri da jinƙai. Abin ban mamaki, har yanzu yana zaune a tsakaninmu a yau (Afis. 2:18–22).
An fara wallafa wannan talifi ne a shafin Blog na Ministirin Ligonier. [Blog ɗin Ministirin Ligonier]


