Abubuwa 3 Da Ya Kamata Ku Sani Game da Kolosiyawa
29/01/2026
Abubuwa 3 Da Ya Kamata Ku Sani Game da Nahum
05/02/2026
Abubuwa 3 Da Ya Kamata Ku Sani Game da Kolosiyawa
29/01/2026
Abubuwa 3 Da Ya Kamata Ku Sani Game da Nahum
05/02/2026

Abubuwa 3 Da Ya Kamata Ku Sani Game da 2 Bitrus

1. Manzo Bitrus ya yi gargaɗi ga majami’u game da haɗarin koyarwar ƙarya da rashin ibada da take haifarwa.

Bitrus bai ambaci waɗannan malaman ƙarya ba, amma daga cikin maganganunsa a cikin 2 Bitrus 2:1–3, a bayyane yake cewa a da suna cewa su kirista ne waɗanda suka rabu da bangaskiya. Bitrus ya bayayana su a matsayi masu shigo da koyarwar karya masu hallaka, suna musun Ubangiji da suke cewa shi ne ya fanshe su. Haka kuma suna jawo mutane da yawa su bi su, har suna sa a zagi Ubangiji. Irin wannan koyarwa ta karya kan kai ga rayuwar zunbi. Saboda sun bar gaskiya, hukuncin Allah a kansu tabbas ne.

Dangane da wasu shawarwari da Bitrus ya ba mu, yana iya zama cewa waɗannan mutanen sun yi amfani da wasiƙun Bulus ba daidai ba don kare halayen da ba su da alaƙa da Allah (ba bisa doka ba). A cikin 2 Bitrus 2:19, Bitrus ya rubuta, “Suna alƙawarin ‘yanci, amma su kansu bayi ne na lalata.” Manzo ya ci gaba da cewa a cikin 2 Bitrus 3:15–16 akwai wasu abubuwa a cikin wasiƙun Bulus “waɗanda suke da wahalar fahimta, waɗanda jahilai da marasa ƙarfi suka karkatar da su zuwa ga halaka, kamar yadda suke yi da sauran Littattafai.” A bayyane yake, abubuwan da ke cikin wasiƙun Bulus sun gurɓata a zamanin Manzanni, kamar yadda yake a zamaninmu.

2. Bitrus ya yi magana game da masu karatunsa a matsayin suna da matsayi na adalci a gaban Allah ta wurin bangaskiya.

Bitrus ya rubuta, “waɗanda suka sami bangaskiya mai matsayi daidai da namu ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi” (2 Bitrus 1:1). Bangaskiyar da ke ba da irin wannan matsayi kyauta ce daga Allah da aka bayar ta wurin Yesu Kiristi—tushen adalcin Allah—saboda haka wani abu da aka karɓa (Afisawa 2:8–9). Duk waɗanda aka ba su irin wannan bangaskiya ana cewa suna da irin wannan bangaskiyar kamar “namu” (Manzanni). Masu bi suna samun wannan matsayi na adalci a gaban Allah ta hanyar kayan aikin bangaskiya ta hanyar Yesu Kiristi—wanda, Bitrus ya gaya mana, Allah ne.

An bambanta wannan matsayin adalci a cikin daidaiton Bitrus na 2 da marasa adalci—malaman ƙarya da waɗanda ke bin su. Sun taɓa sanin hanyar adalci kuma sun yi iƙirarin cewa sun yi imani da bisharar da Bitrus da Manzanni suka yi wa’azi amma tun daga lokacin sun kauce daga gare ta. Bitrus ya rubuta cewa da ya fi musu da ba su taɓa sanin hanyar gaskiya ba (2 Bitrus 2:21), yana kwatanta malaman ƙarya da wani tsarkake a Tsohon Alkawari, wato Nuhu, wanda ya kasance “mai shelar adalci” (2 Bitrus 2:5). Karɓar baiwar bangaskiya ya bambanta masu adalci da waɗanda dole ne su fuskanci hukuncin Allah domin sun kauce daga gaskiya – al’amari ne mai matukar muhimmanci har Bitrus ya yi magana a kai a cikin babi na biyu na wannan wasiƙar.

3. Bitrus ya sanar da mu cewa malaman ƙarya sun musanta cewa Yesu zai dawo.

Bitrus ya riga ya bayyana kasancewa tare da Ubangiji a kan Dutsen Canza Siffa (2 Bitrus 1:16-21), inda ya shaida ɗaukakar Ubangiji. Wannan ya zama tushen amincewar Bitrus ga alkawuran Ubangiji.

A cikin 2 Bitrus 3:3–7, Bitrus ya yi wa masu karatunsa gargaɗi, yana cewa:

Masu ba’a za su zo a cikin kwanaki na ƙarshe da ba’a, suna bin sha’awarsu ta zunubi. Za su ce, “Ina alkawarin zuwansa yake? Tun lokacin da ubanni suka yi barci, komai yana ci gaba kamar yadda yake tun farkon halitta.”

Bitrus ya yi gargaɗin cewa duniyar da ta wanzu tun da daɗewa (a zamanin Nuhu) ruwa ya rufe ta gaba daya, ta kuma hallaka. Ta wannan kalma daya kuma, sammai da kasa da suke wanzuwa yanzu an tanade su domin wuta, ana kiyaye su har zuwa ranar hukunci da halakar marasa tsoron Allah.

Ruɗani game da dawowar Ubangijinmu ya zama ruwan dare a cikin ikklisiyar farko (mutum zai iya tunanin tambayoyi da amsoshi game da ƙarshen zamani a cikin wasiƙun Bulus guda biyu na Tasalonika), kamar yadda yake a zamaninmu. Kwararu a wajen annabcin Littafi Mai Tarki sun yi annabce-annabce (hasashe) masu yawa na banza game da dawowar Yesu Almasihu na biyu, har hakan ya sa mutane da ba Krista ba sun daina kula da koyarwa Littafi Mai Tsarki  cewa Yesu zai dawo domin tayar da matatu, ya yi wa duniya hukunci, ya kuma sabunta kome.

Domin ya ta’azantar da masu sauraronsa, Bitrus ya tunatar da su:

Ubangiji ba ya jinkirin cika alkawarinsa kamar yadda wasu ke ɗaukar jinkirin, amma yana haƙuri a gare ku, ba ya fatan kowa ya halaka, amma kowa ya kai ga tuba. Amma ranar Ubangiji za ta zo kamar ɓarawo, sa’an nan sammai za su shuɗe da ƙara, za a ƙone jikin sama su narke, duniya da ayyukan da ake yi a kanta kuma za a fallasa su. (2 Bitrus 3:9-10) Don haka, in ji Bitrus, bari a yi gargaɗi ga masu ba’a yayin da mutanen Allah ke da begen ɗaukakar da za ta zo, domin “bisa ga alkawarinsa muna jiran sabbin sammai da sabuwar duniya inda adalci ke zaune” (2 Bitrus 3:13).


Wannan labarin wani ɓangare ne na tarin Kowane Littafi na Littafi Mai Tsarki: Abubuwa 3 da Ya Kamata Ku Sani

Kim Riddlebarger
Kim Riddlebarger
Dr. Kim Riddlebarger farfesa ne mai ziyara a fannin tauhidi na tsarin ilimi a Westminster Seminary California kuma fasto mai ritaya na ikklisiyar Christ Reformed da ke Anaheim, Calif. Shi ne marubucin littattafai da dama, ciki har da “A Case for Amillennialism and First Corinthisans” cikin jerin Lectio Continua.