Halayen Ƙauna

25/08/2026

Halayen Ƙauna

25/08/2026

Yaushe Yesu ya mutu?

A kowace shekara, Kiristoci a fadin duniya suna bikin Ista, ranar hutu da ke tunawa da tashin Yesu Kristi daga kabari. Mutuwar Yesu Banazare ba wai kawai abin tunawa ne na addini ba, har ma gaskiya ce ta tarihi. Akwai rubuce-rubucen tarihi da dama daga karni na farko da na biyu wadanda ba su cikin Littafi Mai Tsarki, amma suka ambaci Yesu Banazare (kamar rubuce-rubucen Tacitus, Josephus, Philo, da kuma Talmud).

Duk da yake Littafi Mai Tsarki bai lissafa kwanan watan gicciye shi ba yadda muke tsammani a zamanin yau, babu musun lokaci da wurin da abin ya faru. Ta fahimtar yanayin wannan gaskiyar tarihi, muna amfani da irin dabarar da muke amfani da ita wajen amsa tambayar nan, “Shin Yesu ya kasance a cikin kabari har tsawon kwanaki uku?” Mutuwar Yesu Banazare a tarihi sanannen abu ne. An gicciye shi ranar Juma’a, 3 ga Afrilu, shekara ta 33 bayan haihuwar Almasihu (AD 33), kuma ya mutu da karfe 3 na rana, a Golgota, kusa da birnin/wajen kofar birnin Urushalima. Golgota, wanda ke nufin “Wurin Kokon Kai” a harshen Helenanci, wuri ne na gama gari don gicciye masu laifi a hannun Romawa.

Ya kamata a yi la’akari da muhimmancin mutuwar Yesu da ya yi a idon jama’a. Linjila sun bayyana labarin yadda aka kulla makircin kashe Yesu, da kuma yadda aka sake Barabbas – dan fursuna – maimakon Yesu, bisa al’adar sakin fursuna daya a lokacin bikin Idin Ƙetarewa (duba Mat. 27; Mar. 14–15; Luk. 23; Yoh. 11; 19). Pontius Bilatus, gwamna na biyar na Yahudiya, ko dai don an matsa masa ne ko kuma don yana da hannu a makircin, ya ba da umarnin a kashe Yesu nan da nan. An kirkira hanyar kisan ne don kada a bar wani asiri ko shakkar mutuwa, domin ya haɗa da nau’ikan azaba daban-daban har zuwa lokacin halaka, tare da sa hannun taron jama’a wajen kaskantarwa a wannan gagarumin kallo na fili.

Bugu da ƙari, an rubuta lokacin mutuwar Yesu, tare da marubutan Linjila suna bayyana ra’ayoyin ɓarayi biyu da aka gicciye kusa da shi (duba Mat. 27:38–44; Luk. 23:32–43). Kalmomin ƙarshe na Yesu ma an rubuta su, har da, “An gama,” waɗanda aka faɗa tare da kukan ƙarshe sa’ad da ya “ba da ruhunsa” (Yoh. 19:30; duba kuma Mat. 27:50). Markus ya rubuta martanin wani babban mai kallo, babban jami’in soja, wanda ya “ga yadda ya fitar da numfashinsa na ƙarshe,” ya kuma yi kira, “Hakika mutumin nan Ɗan Allah ne!” (Mar. 15:39).

Wasu hujjoji suna ƙalubalantar jerin lokutan mutuwar Yesu da tashinsa daga matattu, har da ra’ayin suma, wanda ke iƙirarin cewa Yesu bai mutu a kan gicciye ba sai dai kawai ya suma ne. Ko da hakan zai yiwu, gaskiyar lokaci tana gaya mana cewa, a wani matsayi, lalle Yesu Banazare ya mutu. Bayanan tarihi da na Linjila suna nuna mahimmancin lokacin da kuma hanyar mutuwar sa a idon jama’a a kan gicciye. Ko da yake mutuwar Yesu ta kasance mai tsanani, ba ta kasance barkatai ba ko kuma a wajen ikon sarauta na Allah; maimakon haka, “A daidai lokacin da ya dace Almasihu ya mutu domin marasa ibada” (Rom. 5:6, an ƙara jaddadawa).

A cikin wannan, mun zo ga fahimtar cewa mutuwar Yesu a kan gicciye ba kawai wani lamari ne na zahiri ba, har ma tana bayyana gaskiyar ruhaniya. Mutuwarsa ta kasance ta musamman a matsayin mutuwar hadaya da ta alkawari. Wannan shi ne bishara. Yesu ba kawai mutumin kirki ba ne ko kuma malami mai hikima; Shi ne Adamu na ƙarshe. Manzo Bulus ya bayyana cewa, “Gama kamar yadda ta wurin rashin biyayyar mutum ɗaya [Adamu] aka sa mutane da yawa su zama masu zunubi, haka kuma ta wurin biyayyar mutum ɗaya [Yesu] za a sa mutane da yawa su zama masu adalci” (Rom. 5:19). Domin Yesu shi ne Allah-mutum—kamar yadda babban jami’in sojan nan ya gane—hadayar da ya yi a cikin jikinsa madawwami ce ga waɗanda suke haɗe da shi.

Mutuwar Yesu Banazare ya kamata ta tada wasu tambayoyi da dama: Wane ne Yesu? Me ya sa duniya har yanzu take magana game da mutuwarsa? Me ya sa ma kowane abu mai rai yake karkashin ikon mutuwa? Littafi Mai Tsarki ya amsa dukan waɗannan tambayoyi kuma ya taimake mu mu yi tunani a kan mutuwar kanmu. Hoton gicciye yana tilasta mana mu gane cewa ko da yake ba za a taɓa yanke mana hukuncin laifi a gaban kotu ba, har yanzu an riga an yanke mana hukuncin mutuwa. Ko da yake muna iya yin iya ƙoƙarinmu don musanta cewa mu masu mutuwa ne, babu abin da ya kai barazanar mutuwar da ba a zato ba don ya sa mu amince da raunin rayuwa da kuma rashin ikonmu na yin cikakken shiri don ƙarshenta. Dole ne mu zama masu gaskiya ga kanmu kamar yadda Allah Mahaliccinmu ya kasance mai gaskiya gare mu: “Ladan zunubi mutuwa ne” (Rom. 6:23). A cikin wannan, muna farin ciki da mutuwar Almasihu domin “saboda mu [Allah] ya sanya shi ya zama zunubi, shi wanda bai san zunubi ba, domin a cikinsa mu zama adalcin Allah” (2 Kor. 5:21).


An fara wallafa wannan talifi ne a shafin Blog na Ministirin Ligonier. [Blog ɗin Ministirin Ligonier]

Meredith Lee Myers

Meredith Lee Myers

Meredith Lee Myers edita ce ta yanar gizo don Tabletalk da Ligonier Ministries, kuma wadda ta kammala karatu ce a Erskine Theological Seminary a Columbia, SC.