Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Tauhidin Alkawari
20/01/2026
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Yanke shawara bisa Littafi Mai Tsarki
27/01/2026
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Tauhidin Alkawari
20/01/2026
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Yanke shawara bisa Littafi Mai Tsarki
27/01/2026

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Jahannama

Domin kuwa batun jahannama yana da wuyar fahimta, mutane da yawa a ciki da wajen ikklisiya sun yi ƙoƙarin sassauta ra’ayin, domin ta yaya Allah mai ƙauna zai iya tura mutane zuwa irin wannan wuri mai azaba? Amma Allah bai nemi mu kare Shi ko mu warware wannan matsala a madadinsa ba, kuma bai yarda da irin wannan sassautawa ba. Yawancin abin da muka koya game da jahannama, a zahiri, ya fito ne daga Yesu mai ƙauna da kansa, wanda koyarwarsa game da jahannama ta kara faɗaɗa koyarwar Tsohon Alkawari. Ga abubuwa biyar da za a sani game da jahannama.

1. Jahannama wuri ne na gaske na baƙin ciki da rashin iyaka.

Koyarwar da ba daidai ba da aka sani da halakarwa, ko rashin mutuwa ta sharaɗi, ta nuna cewa ana halaka miyagu a hukunci na ƙarshe. Ba sa buƙatar damuwa game da azabar da ke cikin rai bayan mutuwa. Sabanin wannan ra’ayi shine, Littafi Mai Tsarki ya gabatar da jahannama a matsayin wurin baƙin ciki da na har abada. Azaban jahannama ba su ƙarewa (Yahuda 13; Ru’ya ta Yohanna 20:10). Misali, a cikin Luka 16, an kwatanta mai arzikin a matsayin “yana cikin azaba” (Luka 16:23) a cikin Hades kuma yana sane da halin da yake ciki na baƙin ciki, babu shakka ya fi son ya rasa rayuwarsa fiye da ci gaba da azaba.

Haka kuma babu wata hujja na Littafi Mai Tsarki game da “dama ta biyu.” Matsayin zama na mazauna jahannama an tabbatar da shi har abada. Mutuwa ita ce alamar canjin matsuguni dindindin. Saboda haka, ra’ayoyi da ke cewa za a halaka gaba daya rayukan da ke cikin jahannama a ƙarshe (annihalionism) ko kuna cewa za a ba su dama ta biyu ba su da wata hujja daga Littafi Mai Tsarki.

2. Jahannama tana ɗaya daga cikin wurare biyu kawai da kowane ɗan adam zai iya zuwa.

Idan mutum ya mutu, ana binne gawarsa kuma nan take za a kai ransa zuwa gaban Allah, inda ko dai za a kai shi sama ko kuma a jefa shi cikin jahannama. Bayanin Imani na Westminster 32.1 ya bayyana hakan ta wannan hanya:

Jikin mutane, bayan mutuwa, yana komawa ƙura, yana ganin ruɓewa: amma rayukansu, waɗanda ba sa mutuwa ko barci, suna da rayuwa marar mutuwa, suna komawa nan da nan ga Allah wanda ya ba su: rayukan masu adalci, waɗanda aka kammala su cikin tsarki, ana karɓar su zuwa cikin sammai mafi girma, inda suke ganin fuskar Allah, cikin haske da ɗaukaka, suna jiran cikakken fansar jikinsu. Kuma ana jefa rayukan miyagu cikin jahannama, inda suke zama cikin azaba da duhu, an ajiye su zuwa ga hukuncin babban rana. Banda wadannan wurare biyu, Littafi Mai Tsarki bai yarda da wani wuri ba ga rayukan da suka rabu da jikinsu.

A ranar ƙarshe, kowace rai za ta sake haɗuwa da jikinta. A wannan lokacin, masu adalci za su shiga rai madawwami, amma mugaye za a jefa sucikin “azaba ta har abada” (WCF 33.2). Kuma, ban da waɗannan wurare biyu, ga rayuka da suka sake haɗuwa da jikinsu a lokacin tashin matattu, Littafi Mai Tsarki bai yarda da wani wuri ba.

3. Jahannama wuri ne na kasancewar Allah mai fushi.

An bayyana “azabar har abada” ta jahannama a cikin Westminster Confession 33.2 a matsayin wurin hukunci “tare da halaka ta har abada daga gaban Ubangiji, da kuma daga ɗaukakar ikonsa.” Sau da yawa, ana ɗaukar jahannama a matsayin wurin rabuwa da kasancewar Allah. Amma Allah yana ko’ina—ba zai iya kasa kasancewa a wani wuri ba. Maimakon haka, Nassosi suna ɗaukar jahannama a matsayin abin da ba ya faruwa ba na rashin kasancewarsa amma Kasancewa a cikin fushin sa, rashin jin daɗinsa da azabarsa marar iyaka. Allahnmu, wanda shi “wuta ce mai cinye komai” (Ibran. 12:29), zai zubar da “fushinsa da hasalarsa” (Rom. 2:8) akan miyagu a cikin wuta jahannama. 

Idan wannan ya yi muni a kunnen Krista, Hakan saboda yana nuna wani ɓangaren Allah wanda bai yi daidai yadda muke sanin Allah a matsayin ‘ya’yansa ƙaunatattu ba. Abin da miyagu za su fuskanta a jahannama shine fushin Allah wanda Almasihu ya kashe wa mutanensa, amma gaskiyar jahannama ga waɗanda aka ƙi sun fi baƙin ciki fiye da ma bayanin alama game da shi, kamar yadda kowace alama za ta iya wakilta da kuma nuna gaskiya ba tare da cikakke ba. Wataƙila bayanin alama na Littafi Mai Tsarki game da jahannama ya faru ne saboda gaskiyar cewa azabar da ba ta ƙarewa daga Allah mai tsarki ba ta da muni sosai.

4. Mazauna Jahannama ne suka zabi kasancewar su a wurin.

Jahannama ita ce wurin da waɗanda suka zaɓi su ƙaunaci duhu maimakon haske za su je (Yahaya 3:18–21). Wannan zai iya zama kamar ya saba wa kukan mai arzikin, “Baba Ibrahim, ka yi mini jinƙai, ka aiko Li’azaru ya tsoma ƙarshen yatsansa a cikin ruwa ya sanyaya harshena, gama ina cikin damuwa a cikin wannan harshen wuta” (Luka 16:24). Amma a lura ba kawai ne mai arziki a gushe yana son Allah ba, yana son sauki daga azabar Allah.

Masu bin Calvinism Sun yardacewa kowane mutum a ƙarshe zai sami abin da ya zaɓa da yardar rai—ko dai don bauta wa Allah ta hanyar sake farfaɗo ta Ruhu Mai Tsarki ko kuma su la’anci Allah. Wadanda suke cikin jahannama ba za su iya, kuma ba za su taba zargin rashin adalci ba, domin an basu dadai abin da ya dace da su, kuma abin da su kansu suka zaba. Littafi Mai Tsarki bai ga saɓani a cikin jahannama ba cewa azaba ce da Allah ke yi wa miyagu kuma jahannama ita ce wurin da mutane suka zaɓa da yardar rai. Jahannama, to, ita ce “ba da kanmu” ga sha’awarmu da sha’awar jiki (Romawa 1:24).

5. Jahannama ta yi daidai da yanayin Allah.

Jahannama ba Abin kunya ba ce ga Allah. Ba wani aiki mai kunya ba ne a cikin tarihinsa wanda ya saba wa ainihin wanda yake. A’a, jahannama ta yi daidai da adalcin Allah mai tsarki wanda ke buƙatar a daidaita hukuncin zunubi da laifin wanda ake zargi. Adalcin Allah da jinkai sa ba halaye ne na daban ba. Suna da daidaito daidai, kuma sama da jahannama suna nuna wannan jituwa mai tsarki. Da Allah ba adalci ba ne, halakarwa, ko kuma duk wani ra’ayi da bai shafi Littafi Mai Tsarki ba da ya shafi rayuwar bayan mutuwa zai kasance a cikin yanayin yiwuwar.

Ka yi la’akari da alheri da adalcin Allah a cikin aikin Ɗansa. Shin aikin Kristi ba zai zama banza ba idan babu jahannama? Idan ba a hallaka mugaye ba ko kuma ba a bari su shiga sama ta wani hanya ba, shin ba za a ce hadaya da Almasihu ya yi ta zama banza ba? Hakika, ƙin jahannama ba wai kawai ya saba wa halin Allah ba ne, amma yana daidai da tattaka Ɗan Allah a ƙarƙashin ƙafa (Ibran. 10:29). Halin Allah—duka adalcinsa da nagartarsa—yana buƙatar aiwatar da cikakken hukunci na zunubi ga miyagu har abada.

Ko da yake za a iya faɗin abubuwa da yawa game da jahannama, wataƙila ya kamata mu tuna cewa bayanin Littafi Mai Tsarki game da jahannama an yi shi ne don ɗaukaka alherin Kristi wanda ya cece mu daga gare ta, da kuma ƙarfafa himma a cikinmu don gargaɗin wasu su gudu daga azabar jahannama ta hanyar komawa ga Kristi cikin bangaskiya da tuba ta gaskiya.


Wannan labarin wani ɓangare ne na tarin Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani

Aaron Garriot
Aaron Garriot
Rev. Aaron L. Garriott shine babban editan mujallar Tabletalk , farfesa mai kula da Reformation Bible College da ke Sanford, Florida, kuma ya kammala karatunsa a Kwalejin Wheaton da Reformed Theological Seminary da ke Orlando, Florida. Dattijo ne mai koyarwa da aka naɗa a ikklisiya Presbyterian a Amurka.