
Abubuwa 3 da Ya Kamata Ku Sani Game da Yunusa
05/03/2026Abubuwa 3 da Ya Kamata Ku Sani Game da Ezra
Littafin Ezra, tare da littafin Nehemiya, ya ƙunshi kimanin shekaru ɗari na tarihin Isra’ila, tun daga lokacin da Sairus ya yi umarni a shekara ta 538 BC (kafin haihuwar Annabi Isa) wanda ya ba Yahudawa damar komawa ƙasarsu ta Urushalima da Yahuda, zuwa lokacin da Nehemiya ya dawo Urushalima a shekara ta 433–432 BC. Abubuwan da suka faru sun taru a kusan manyan lokuta biyu a cikin wannan tsawon shekaru ɗari—538–515 BC (Ezra 1–6) da 458–433 BC (Ezra 7–Neh. 13). Tsohon lokacin ya mayar da hankali kan sake gina haikalin. Lokacin na ƙarshe ya mayar da hankali kan gyara mutane ta hanyar Dokar da ke ƙarƙashin jagorancin Ezra da sake gina katanga a ƙarƙashin jagorancin Nehemiya. Waɗannan lokutan sun ci gaba da ciyar da labarin alkawari gaba kuma sun shirya duniya don isowar Wanda aka yi Alƙawari, Yesu Almasihu. Idan ka yi tunani game da littafin Ezra, ga abubuwa uku da ya kamata ka sani.
1. Akwai Sarki mafi girma da alheri fiye da Sairus wanda ya yi shelar shekarar ‘yanci ga mutanen Allah.
A cikin farkon surori na Ezra, mun koyi game da wani lokaci a rayuwar mutanen Allah lokacin da aka kore su daga ƙasarsu tsawon shekaru saba’in saboda zunubinsu. Amma Allah ya motsa zuciyar wani sarki na Farisa ya ‘yantar da su kuma ya motsa zukatan mutanensa su koma gida don sake gina haikalin Allah wanda wani sarki arna ya lalata shekaru saba’in da suka gabata. Labari ne mai ban mamaki, wanda ke cike da bala’i da alƙawarin Allah; bala’i da farin ciki; tsoro da bangaskiya; yanayi mai wahala da bege; cikas a hanya da ceton Allah; wahala da ceto; rawar jiki da aminci; damuwa da mamaki.
Ubangiji wanda ya tada Sairus da waɗanda suka dawo a lokacinsa cikakke shi ma ya aiko Ɗansa a cikin cikakken lokacinsa “don ya ‘yantar da waɗanda ake zalunta, ya yi shelar shekarar alherin Ubangiji” (Luka 4:18-19). Shi ma yana kan yanayinku a yau. Yana sanya ku a wurin da ya dace a daidaicin lokaci. Kuna iya duban gaba da bege, kuna sane da cewa ko yanzu yana amfani da matsalolinku don jawo ku zuwa gare Shi da kuma ɗaukaka sunansa mai girma. Bari mu mayar da martani ga ‘yancinmu cikin Almasihu da zuciya mai juyawa zuwa ga hidima da sadaukarwa. Bari mu nuna ƙaunarmu ga Allah ta hanyar bauta masa da kuma yin aiki don ɗaukakarsa.
2. Haikalin da aka sake ginawa ya kansance kawai inuwa ce ta anihin Haikalin da ke zuwa, wato Yesu Kristi, kuma adawar da mutanen Allah suka fuskanta wajen sake gina shi ta nuna babbar adawar da Kristi zai fuskanta a lokacin rayuwarsa da hidimarsa.
Littafin Ezra ya ta’azantar da mutanen Allah ta hanyar tunatar da su amincin Allah ga alkawuransa. Hakanan yana ƙalubalantar mutanen Allah su kasance masu aminci ga Allah a cikin mawuyacin lokaci. Ta hanyar hawaye da karaya, muna duban Mai Cetonmu wanda ya sha wahala dominmu ta hanyar bin sawunSa da kuma neman Ya dawo cikin ɗaukaka. Wata rana kwarin yanke ƙauna zai zama dutsen farin ciki na har abada inda za mu bauta wa Ubangijinmu da Mai Cetonmu har abada a cikin birnin da zai zo. Ya kamata masu bi su yi tsammanin wahala yayin da suke aiki don ɗaukakar Allah kuma su dogara gare Shi a lokutan da ke sa su karaya. Ya kamata mu ba da albarkatunmu ga waɗanda ke yin aikin Ubangiji da farin ciki, mu haɗu tare da mutanen Allah don yin hidima cikin sunan Kristi, mu yi wa masu bi da aka tsananta wa waɗanda aka tilasta musu dakatar da aikin mulki, da kuma ƙarfafa waɗanda ke cikin aikin bishara.
3. Allah cikin kulawarsa yana tsara dukan abubuwa domin daukakarsa da kuma nufinsa na fansa.
Waɗanda suka dawo daga bauta sun dakatar da aikin gina haikalin saboda yanayin da ke hana su jin daɗi. Amma annabawan Allah sun tunatar da su maganar Allah. Cikin shekaru huɗu Allah ya tsara abubuwa cikin tsari har aka kammala haikalinsa, aka kuma sake gina bauta. Labari ne na alheri mai ban mamaki, tanadi, da farin ciki. Saboda haka, yana tunatar da mu cewa lokacin da muka karaya kuma muka jarabtu mu dakatar da aikin da Allah ya kira mu zuwa gare shi, dole ne mu juya ga Kalmar Allah don gaskiya, mu huta cikin Almasihu mu yi tafiya cikin hanyoyinsa domin mu ji daɗin cikar farin ciki, kuma mu dogara ga manufofin Allah na tanadi don haɗa komai don amfanin mu da ɗaukakarsa. Cikakkiyar farin cikinmu ta fito ne daga haɗin kanmu da Kristi da kuma biyayyarmu ga Kalmarsa. Dangane da wannan, ya kamata mu tallafa wa wasu a cikin aikin mulki da kalmomin Littafi Mai Tsarki da addu’a, mu yi aiki tuƙuru a wuraren da Allah ya kira mu, mu koya wa wasu cewa zama cikin Almasihu yana haifar da farin ciki, kuma mu ci gaba da yin ibada tare. Shekaru da yawa bayan Ezra firist ya yi tafiyar komawa Urushalima, wani firist ya yi tafiya zuwa Urushalima. Amma wannan firist ya zo daga sama zuwa duniya domin ya tabbatar da fansar mutanen Allah da hadayar kansa. Domin hadayarsa ta kasance cikakke kuma ta ƙarshe a kan gicciye, ni da kai za mu iya kusantar kursiyin alheri da amincewa, muna roƙon Allahnmu da ƙarfin hali ya kare mu, ya azurta mu, kuma ya cika manufofinsa a gare mu. Littafin Ezra yana ƙarfafa mu mu ci gaba da aikin alherin da Firist da Sarki suka kira mu mu yi yayin da muke dogara ga shirye-shiryensa na alheri, kariya, da tanadinsa.
Wannan labarin ɓangare ne na tarin Kowane Littafi na Littafi Mai Tsarki: Abubuwa 3 da Ya Kamata a Sani


